Isa ga babban shafi
Algeria

Shugaba Bouteflika zai yi takarar shugabancin kasar Aljeriya

Yau Asabar Priministan kasar Algeria Abdelmalek Sellal, ya ce shugaban kasa Abdelaziz Bouteflika zai yi takarar shugabancin kasar, da za a yi a watan Aprilu mai zuwa. Sellal ya fadi haka ne lokacin da yake hira da manema labaru a yayin wani taron tattalin arzikin kasar da ake yi a birnin Oran, da ke yamma da birnin Algiers.Kafafen yada labarum kasar sun ce gobe Lahadi shugaban, mai shekaru 76 a duniya zai karbi takardun neman tsayawa takarar, da ma’aikatar harkokin cikin gidan kasar.A bara shugaba Bouteflika ya yi fama da ciwon bugun zuciya, inda ya shafe watanni 3 a wani asibitin kasar Faransa. 

Shugaban kasar Algeria, Abdoulaziz Bouteflika
Shugaban kasar Algeria, Abdoulaziz Bouteflika english.ahram.org.eg
Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.