Isa ga babban shafi
Cote d'Ivoire

Matan shugabannin Burkina Faso da Cote D’Ivoire sun kaddamar da yaki akan safarar yara

Matan shugabannin kasashen Burkina Faso da kuma Cote D’Ivoire, sun kaddamar da wani shiri domin yaki da matsalar safarar yara kanana da ke ci gaba da yin kamari a tsakanin kasashensu.

Wasu yara a wani taron da kungiyar Save the Children ta shirya a Mozambique
Wasu yara a wani taron da kungiyar Save the Children ta shirya a Mozambique
Talla

Chantal Compaore da kuma Dominique Ouattara, sun bayyana aniyarsu ta yaki da wannan matsala a tsakanin kasashen, inda aka ce akalla yara kanana dubu 1,895 ne aka tsallaka iyakokinsu da su a cikin shekarar da ta gabata kawai.

Kasar Cote D’Ivoire ta kasance wani dandali na na safarar yara kanana inda ake shigo da yara kanana daga kasashen Mali da Burkina Faso.

Shirin matan shugabannin a cewar rahotanni zai fadada irin matakan da ake da su a kasa na yaki da wannan matsalar.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.