Paris Saint Germain ta lashe gasar Ligue 1 ta Faransa kafin karkarewa
Kungiyar kwallon kafa ta Paris Saint Germain ta lashe gasar Ligue 1 ta Faransa a bana, tun kafin a kai ga karkare gasar da tazarar maki 13, tsakaninta da ta biyu a saman Teburin.
Wallafawa ranar:
Nasarar ta PSG na zuwa ne bayan ta biyu a teburin gasar Monaco ta yi rashin nasara da ci 3 da 2 a gidan Lyon ranar Lahadi.
Yanzu haka dai saura wasanni uku kafin karkare gasar ta kakar nan, kuma nasarar da ta yi na nufin ta lashe kambun gasar har sau 12 kenan a tarihi.
Wasu dai na ganin tun a ranar Asabar din da ta gabata ya kamata PSG din ta lashe kofin, amma sai ta tashi 3 da 3 a gida a wasan da suka fafata na mako na 31 da Le Havre.
Jumulla wannan shi ne kofin Ligue 1 da Paris Saint Germain ta dauka karo na 10 cikin kakar wasanni 11 da suka gabata.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu