Isa ga babban shafi
Faransa

Valls ya kafa sabuwar gwamnati a Faransa

Sabon Firaministan kasar Faransa Manuel Valls ya sanar da kafa majalisar ministoci, kwana daya bayan da ya karbi ragamar tafiyar da wannan mukami daga hannun wanda ya gabace shi Jean-Marc Ayrault.

Shugaba Francois Hollande da Firaministansa Manuel Valls
Shugaba Francois Hollande da Firaministansa Manuel Valls REUTERS/Philippe Wojazer
Talla

Wasu daga cikin sabbin fuskoki a wannan gwamnati har da Segolene Royal wadda aka bai wa mukamin ministan kare muhalli, yayin da ministan tsaro da na harkokin waje a gwmanatin da ta gabata, Jean-Yves le Drian da kuma Laurent Fabius za su ci gaba da rike mukamansu.

A ranar talata ta makon gobe ce Manuel Valls zai je gaban Majalisar Dokokin kasar domin salon siyararsa a gaban majalisar.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.