Shirin Lafiya Jari Ce tare da Azima Bashir Aminu ya yi nazari ne kan sake bazuwar cutar kuturta a Najeriya, inda Majalisar Dinkin Duniya ta ce, kasar ce ke kan gaba wajen yawan kutare a kasashen Afrika.
Alkaluman Majalissar Dinkin Duniya sun nuna cewa, akwai kutare kimanin dubu 3 da 500 yanzu haka a Najeriya, abin da ya sa kasar ke kan gaba a nahiyar Afrika, a daidai lokacin da ake ci gaba da yakin kawar da wannan lalura daga dora-duniya.
Shirin na Lafiya Jari Ce ya kuma yi nazari kan yadda za a iya magance cutar kuturta da zaran alamominta sun fara bayyana.Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu