Isa ga babban shafi

Lauyoyin Bazoum sun musanta zargin yunkurin tserewa da ake masa

Lauyoyi hambararren shugaban Jamhuriyar Nijar, sun bukaci a sake shi ba tare da bata  lokaci ba, kwana guda bayan sojojin da ke mulkin kasar suka ce  sun dakile wani  yunkurin tserewa da ya yi tare da iyalansa, kusan watanni 3 bayan daurin talala da aka masa.

Hambaraarren shugaban Nijar, Mohamed Bazoum,
Hambaraarren shugaban Nijar, Mohamed Bazoum, © RFI/France 24
Talla

Ana tsare da Mohamed Bazoum, matarsa da dansa ne ba tare da  an bari sun leka waje ko kuma an bari sun gana da lauyoyinsu ba, kamar  yadda  wata  tawagar lauyoyin kasa da kasa da ke wakiltar  Bazoum din suka bayyana a  wata sanarwa, suna mai musanta  zargin yunkurin tserewa da masu juyin mulkin suka ce ya  yi.

Hambararren shugaban da mai dakinsa sun kasance   karkashin daurin talala ne tun a karshen watan Yuli da aka kifar da gwamnatin farar  hula, kuma an yanke musu lantarki da ruwa.

Tun bayan wannan juyin mulkin ne kungiyar ECOWAS/CEDEAO ta shiga takun saka da sojojin da suka  kifar da gwamnatin Bazoum na Nijar, lamarin da ya kai ga rufe iyakokin kasar da makwaftanta, har ma Najeriya ta katse mata wutar lantarki.

Zalika, juyin mulkin ya janyo baraka tsakanin Nijar  da tsohuwar uwargijiyarta Faransa, inda har sojojnda suka yi juyin mulkin suka sallame jakadanta da dakarun kasar.

Har yanzu dai babu wani ci gaba a game da yunkurin lalubo masalaha a  kan wannan dambarwa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.