Za mu jajirce har sai an yi wa mutanen Tudun-Biri adalci - Sarkin Musulmi
Mai Alfarma Sarkin Musulmi na Najeriya, Muhammad Sa'ad Abubakar ya bukaci a yi adalci ga mutanen da harin sojin kasar ya kashe a garin Tudun-Biri da ke kauyen Karamar Hukumar Igabi ta jihar Kaduna, inda sama da rayuka 100 suka salwanta.
Wallafawa ranar:
Sarkin ya fadi haka ne a wurin taron murnar cika shekaru 25 da darewar Sarkin Jama'a Alhaji Muhammad Isa Muhammad kan karagar mulki a fadarsa da ke garin Kafanchan a jihar Kaduna a wannan Juma'ar.
Ba wai kawai taron taya sarki murna ba ne ya kawo mu nan, har da yin addu'a ga masarautar da kuma rayukan mutanen da suka salwanta a Kaduna. Za mu yi matsin lamba don ganin an yi adalci ga mutanen. Inji Sarkin Musulmin.
Wannan na zuwa ne bayan jama'a da dama a Najeriya sun yi ta korafi kan cewa, ba su komai daga bakin Sarkin Musulmin ba tun bayan aukuwar harin na kuskure kan mutanen da ke halartar taron maulidi a garin na Tudun-Biri.
Tuni gwamnatin Najeriya ta bayyana cewa, lallai za a hukunta duk wanda ke da hannu a wannan harin, inda har mataimakin shugaban kasar, Kashim Shettima ya ziyarci mutanen da ibtila'in ya shafa a asibitin Barau Dikko da ke Kaduna.
Mataimakin shugaban kasar ya sanar da shirin gwamnatin tarayya na sake gina garin na Tudun-Biri da kuma ba su tallafi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu