Cutar sankarau ta kashe sama da mutane 20 a jihohi 3 na Najeriya
A Najeriya an samu Karin mutane 23 da suka mutu sakamakon harbuwa da cutar sankarau, tare da 212 da aka tabbatar sun harbu da cutar a cikin jihohi 3 na kasar.
Wallafawa ranar:
A wani sabon rahoto da ta fitar a jiya Asabar, cibiyar yaki da cutuka ta kasar ta ce adadin wadanda suke harbuwa d cutar a duk mako a lokacin da ta yi bincikenta daga 27 ga watan Maris zuwa 2 ga Afrilu sun kai kaso 8.
Rahoton na cibiyar ya nuna cewa jihar Jigaawa a arewa maso yammacin kasar ce ke da kaso 62 na wadanda suka harbu da wannan cuta, a yayin da Yobe da Adamawa a arewa maso gabashin kasar, inda aka samu mutane 4 da suka harbu da cutar a kowannensu na da kaso 17.
Cibiyar ta ce daga cikin mutane 23 da suka mutu sakamakon cutar, 17 daga Yobe ne, a yayin da 9 suka mutu a Jigawa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu