Kaduna ta sanya dokar hana fita a kananan hukumomin Kaura da Jama'a
Gwamnatin jihar Kaduna ta sanya dokar hana fita ta sa’o’I 24 a kananan hukumomin Jama’a da Kaura a wani yunkuri na kwantar da hankulan jama’a biyo bayan tarzomar da ta hallaka mutane da dama.
Wallafawa ranar:
Kwamishinan tsaron cikin gida Samuel Aruwan ya ce matakin ya biyo bayan shawarwarin masana tsaro biyo bayan tarzomar.
Aruwan ya shaidawa manema labarai cewa, jami’an tsaro za su tabbatar da doka da oda a yankunan da tarzomar ta faru.
Rahotanni sun ce tun farko wasu fusatattun matasa ne suka farwa matafiya bayan kisan wani magidanci a Kafanchan.
Gwamnatin jihar ta Kaduna ta baki Samuel Aruwan ya roki al’umma su bi umarnin don tabbatar da tsaro da rayukan al’umma a kananan hukumomin biyu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu