'Yan bindiga sun kashe malamin makaranta a Kaduna
‘Yan bindiga sun kashe wani malamin makaranta tare da wasu mutane 4 a unguwar Layin lasan ta karamar hukumar Birnin Gwari a jihar kaduna da ke arewa maso yammacin Najeriya.
Wallafawa ranar:
Wannan na kunshe ne a wata sanarwa da kungiyar kyautata tsaro da shugabanci na gari ta Birnin gwari, wadda kuma ta samu sa hannun shugabanta Ibrahim Abubakar Nagwari.
Zalika rahotanni sun ce ‘yan bindigar sun yi awon gaba da mutane 16 a Dogon Dawa, layin mahuta da kuma kauyukan Tabanni a gabashin karamar hukumar.
Sanarwar ta ce lamarin ya auku ne a mabanbantan lokutaa cikin kwanaki 4 da suka wuce, tana mai cewa an kashe Haruna Tanko, wanda malamin makaranta ne tare da wasu mutane 4.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu