Isa ga babban shafi
Najeriya - Kaduna

‘Yan bindiga sun saki karin daliban sakandaren Bethel Baptist

‘Yan bindiga sun saki karin dalibai 10 da suka sace daga makarantar sakandare ta Bethel Baptist da ke jihar Kaduna.

Allon makarantar Bethel Baptist da 'yan bindiga suka sacewa dalibai 121 a karamar hukumar Chikun dake jihar Kaduna.
Allon makarantar Bethel Baptist da 'yan bindiga suka sacewa dalibai 121 a karamar hukumar Chikun dake jihar Kaduna. © AP
Talla

Daliban sun sake samun 'yanci ne a jiya Asabar, bayan sun shafe kimanin kwanaki 75 a hannun ‘yan binidgar da suka yi garkuwa dasu.

An sace daliban ne dai tun ranar 5 ga watan Yuli lokacin da gungun ‘yan bindiga suka kaiwa makarantar ta Bethel Baptist farmaki a karamar hukumar Chikun da ke Kaduna.

Iyayen daliban makarantar sakandaren Bethel Baptist da ‘yan bindiga suka sace yayin addu'ar dawowar yaran nasu a jihar Kaduna da ke arewa maso yammacin Najeriya. 14 ga Yuli, 2021.
Iyayen daliban makarantar sakandaren Bethel Baptist da ‘yan bindiga suka sace yayin addu'ar dawowar yaran nasu a jihar Kaduna da ke arewa maso yammacin Najeriya. 14 ga Yuli, 2021. Kola Sulaimon AFP

Wani babban jami’I a makarantar ya shaidawa manema labarai cewa an saki daliban ne bayan biyan kudaden fansar da ba a bayyana adadinsu ba.

Karin daliban 10 da suka samu 'yanci, ya sanya a halin yanzu adadin wadanda ‘yan bindigar suka saki kaiwa 100 daga cikin 121 da suka sace a watan Yuli.

Da fari dai 'yan bindigar sun saki daliban 28 ne a ranar 25 ga watan Yuli, bayan da aka ce an biya su kudin fansa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.