'Yan bindiga a Kaduna sun saki daliban makarantar Bethel Baptist 32
Rahotanni daga Najeriya na cewa karin dalibai 32 na makarantar Bethel Baptist High School dake Kaduna, suka samun 'yanci daga hannun 'yan bindiga masu garkuwa da mutane.
Wallafawa ranar:
Joseph Hayab, Shugaban kungiyar Kiristocin Najeriya (CAN) reshen jihar Kaduna, ya tabbatar da sakin daliban a ranar Juma’a.
Hayab, wanda ya ce tuni aka hada daliban da iyayensu, bai yi cikakken bayani ba dangane da yanayin sakinsu ba. To said ai har yanzu akwai sauran daliban makarantar 31 da suka saura a hannun ‘yan bindigar.
Daliban Tegina
Wannan ci gaban na zuwa ne kwana guda bayan da daliban makarantar Salihu Tanko Islmammiya da ke Tegina a jihar Neja suka samu 'yanci bayan shafe kwanaki 88 a hannun masu garkuwa da mutane.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu