Najeriya-Kaduna-'Yan Bindiga
'Yan bindiga sun kashe mutane 3 tare da jikkata da dama a Kaduna
Mutane 3 sun mutu yayin da dama suka jikkata a wani hari da aka kai karamar hukumar Zangon Kataf a da ke jihar Kaduna a Najeriya.
Wallafawa ranar:
Talla
Kwamishinan tsaron cikin gida na jihar, Samuel Aruwan ya tabbatar da aukuwar lamarin a wata sanarwa da ya fitar a Juma’a.
Aruwan ya ce sun samu labarin cewa wasu da ba a san ko su wanene ba sun kai hari a kauyukan Machun da Manuka inda suka kashe mutane uku tare da raunata da dama.
Ya ce ba a fayyace adadin wadanda suka samu rauni ba, amma suna nan suna karbar magani.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu