An dage zabe a kananan hukumomi hudu na Kaduna saboda rashin tsaro
Hukumar zabe mai zaman kanta a Kaduna, ta dage zabukan da aka shirya gudanarsu yau ranar Asabar na sabbin Shugabanni da kuma Kansiloli a wasu kananan Hukumomin jihar hudu.
Wallafawa ranar:
Shugabar Hukumar zaben, Saratu Dikko Audu, ta ce matakin ya biyo bayan rahotannin yiwuwar fuskantar barazanar tsaro da ke cewa ba zai yiwu a gudanar da zabe cikin kwanciyar hankali a wuraren ba.
Kananan hukumomin da dage zaben ya shafa dai sun hada da Birnin Gwari, Chikun, Zangon Kataf da kuma Kajuru.
An sauya ranakun zaben Shugabannin kananan hukumomin da Kansilolin zuwa ranar 25 ga watan Satumban da muke.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu