Isa ga babban shafi
Yemen

Yemen za ta janye jami'an diflomasiyya daga kasar Iran

Gwamnatin kasar Yemen da ke gudun hijira ta bayyana aniyar janye jami’an jakadancinta daga Iran, saboda abinda ta bayyana a matsayin shishshigin da hukumomin birnin Tehran ke yi a harkokin kasar.

Shugaban Yemen, Abd Rabbo Mansour Hadi
Shugaban Yemen, Abd Rabbo Mansour Hadi REUTERS/Khaled Abdullah
Talla

Wata sanarwar da fadar shugaba Abedrabbo Mansour Hadi ta fitar, ta zargin Iran da marawa mayakan Huthi baya, a yakin da suke yi da gwamnatin kasar ta Yemen mai samun goyon bayan kasashen Larawaba.

A karshen watan Maris Shugaba Hadi ya tsere zuwa birnin Riyadh na kasar Saudiyya lokacin da mayakan na Huthi suka nufi inda ya fake a birnin in Aden.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.