Isa ga babban shafi

Kakakin majalisar Cuba na ziyara a Kenya kan makomar likitocin kasar da ke hannun Al-shabab

Kakakin Majalisar Cuba na ziyara a Kenya don tattaunawa game da makomar likitocin kasar 2 da mayakan Alshabaab suka yi garkuwa da su a wani yanki na Nairobi shekaru 5 da suka gabata.

Kakakin majalisar Cuba kenan, Esteban Lazo
Kakakin majalisar Cuba kenan, Esteban Lazo © Wikipedia
Talla

Ma’aikatar harkokin wajen Kenya da ke tabbatar da ziyarar Esteban Lazo na zuwa ne bayan Al-Shabaab ta fitar da wata sanarwa da ke ikirarin cewa likitocin na Cuba biyu sun mutu sun mutu a luguden wutar da Sojin Amurka suka yi a sansanin mayakan kungiyar da ke Somalia cikin makon jiya.

Tun a ranar 12 ga watan Aprilun 2019 ne mayakan Al-Shabaab suka yi garkuwa da likitocin na Cuba guda 2 kuma tun daga wancan lokaci ake tattaunawar kubutar da sub a tare da nasara ba.

Lazo "ya kai ziyara zuwa Kenya domin tattaunawa da manyan hukumomin kasar kan makomar likitocin kasarmu da aka yi garkuwa da su", in ji sanarwar ma’aikatar harkokin wajen Cuba.

Sanarwar ta ce, ma’aikatar harkokin wajen na kan tattaunawa da gwamnatin Somaliya, tare da neman tallafin gwamnatin Amurka a diflomasiyyance.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.