Isa ga babban shafi
Yemen

Mayakan Huthi na neman zaman barazana ga sauran kasashen Duniya

Mayakan Huthis a Yamen na ci gaba da kokarin karbe ikon wuraren bincike dake garin Bab Al-Mandab da ke kudancin kasar, yanzu dai hankula al’ummar kasar a tashe yake, ganin yadda yunkurin mayakan ke barazana ga tsaron kasar dama na sauran kasashen Duniya

Yan tawayen Yemen
Yan tawayen Yemen REUTERS/Nabeel Quaiti
Talla

A jiya lahadi mayakan suka karbe ikon filin jirgin sama dake birnin Taez abinda ke kara barazana ga tsaron Shugaban kasar Abdelrabuh Mansour Hadi da yanzu haka ke samun mafaka a birnin Aden

Shugaba Hadi ya tsere ne daga daurin talala, a makon da ya gabata, kasar Yemen ta fada cikin rikici, sakamakon rarabuwar kawuna tsakanin mayakan Huthis da magoya bayan Shugaban kasar

Yanzu dai masana sun ce idan har mayakan Huthis sun yi nasarar karbe ikon wuraren binciken kan ruwa to hakika kasar zata fada cikin rikicin da zai zama matsala ga sauran kasashen duniya

Masanan sun bayyana dangatakar da mayakan na Huthis ke da Iran wanda acewar su nasarar ga mayakan Huthis nasara ce da kasar Iran zata yi marhabun da ita ganin haka zai taimaka mata a shirin Nukiliyar kasar

Tuni dai kwamitin Sulhu na MDD ya bayyana amincewar sa ga Gwamnatin Shugaban kasar Mansour Hadi da Gwamnatin hadin kan kasar da yanzu haka mayakan houthi ke neman kawar wa.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.