Isa ga babban shafi
Najeriya

Ma'aikatan sa-kai 800 don hana yaduwar Ebola a Lagos

Gwamnatin jihar Lagos da ke tarayyar Najeriya, ta ce yanzu haka ta horas da masu aikin sa-kai akalla 800 domin taimaka wa sauran jami’an kiwon lafiya da ke yaki da cutar Ebola da kawo yanzu ta kashe mutane 4 a birnin.

Dubarun hana yaduar Ebola a Ivory Coast
Dubarun hana yaduar Ebola a Ivory Coast REUTERS
Talla

Mai Magana da yawun gwamnan jihar Lagos Babatunde Raji Fashola, wato Mista Hakeem Bello, ya shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa cewa, yanzu haka an rarraba wadannan ma’aikatan sa-aka zuwa wasu unguwanni 57, to sai dai ya ce har yanzu akwai bukatar karin jama’a a wannan aiki.

Kawo yanzu dai cutar ta Ebola ta yi sanadiyyar mutuwar mutane 1,145 a kasashe 4 na yammacin Afirka ciki har da Najeriya.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.