Isa ga babban shafi
Najeriya

Ebola: Gaisuwa ta fara wahala a Najeriya

A Najeriya, yanzu haka hankulan jama’a sun yi matukar tashi sakamakon yadda cutar nan ta Ebola ta yi sanadiyyar mutuwar mutane hudu, yayin da wasu fiye da dari daya ke ci gaba da kasancewa a karkashin kulawar jami’an kiwon lafiya. A game da yadda cutar ke saurin yaduwa a tsakanin al’umma, wannan ya sa jama’a suka soma nuna kyama ta fanni cudanya ko kuma yin mu’amala a tsakaninsu. Wakilinmu na birnin Kano Abubakar Isa Dandago ya aiko da rahoto.

Ministan Lafiya Onyebuchi Chukwu da karamin Minista Haliru Alhasan suna gaisuwa daga nesa bayan zantawa da manema labarai game da cutar Ebola a Najeriya
Ministan Lafiya Onyebuchi Chukwu da karamin Minista Haliru Alhasan suna gaisuwa daga nesa bayan zantawa da manema labarai game da cutar Ebola a Najeriya The nation, Photo Abayomi Fayese
Talla

02:54

Rahoto: Mu'amula ta fara wahala a Kano

Abubakar Issa Dandago

 

 

 

 

 

Hukumar lafiya ta duniya WHO tace girman Cutar Ebola da ke bazuwa a yammacin Afrika ya zarce tunanin mutane tare da kiran daukar matakan gaggawa domin dakile yaduwar cutar da ta kashe mutane 1,069.

Hukumomin Najeriya sun gana da jami’an hukumar lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya kan annobar cutar Ebola da yanzu haka ta kashe mutane 3 a cikin kasar. Daga Abuja Muhammed Kabir Yusuf ya aiko da Rahoto.

01:31

Rahoton Kabiru Yusuf daga Abuja akan Ebola

Kabir Yusuf

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.