‘Yan bindiga sun sace Uwargidan Mataimakin Firaministan Kamaru
Rahotanni daga Kamaru sun ce wasu ‘Yan bindiga da ake kyautata zaton Mayakan Kungiyar Boko Haram ne sun yi awon gaba da Uwar gidan Mataimakin Firamnistan kasar tare da wani Kaftin na Soja da ke tsaronsa a Kolafata a arewacin kasar, bayan Ministan ya zo bikin sallah a Marwa daga Yawundi.
Wallafawa ranar:
Garin Kolofata dai nan ne Mahaifar Mataimakin Firaminista Ahmadu Ali, kuma tana cikin karamar hukumar Mayo Sava da ke kan iyaka da Najeriya.
Rohotonni sun ce mutani shida suka rasa rayukansu a hare haren da ‘Yan bindigar suka kai.
Minister dai yazo da iyalan sa daga Yawunde don bukukuwan sallah, Amma ya tsira da ransa daga harin. Yanzu haka kuma wakilinmu Ahmed Abba yace Ministan yana garin Marwa Hedikwatar Arewa mai nisa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu