Isa ga babban shafi
Najeriya

An kai harin Bom a Kano

Akalla mutane biyar aka ruwaito sun mutu, Takwas kuma suka jikkata a wani harin bom da aka kai a wani wajen da Kiristoci ke ibada a garin Kano. Wasu Rahotanni daga Kano sun ce wani bom ya tashi da wata Mata da ta je dasa bom din a kofar Nasarawa, a daidai lokacin da Al'ummar Najeriya ke bikin Sallah bayan kammala Azumin Ramadan.

Jami'an tsaron Najeriya a inda aka kai harin Bon a Unguwar Sabon gari a Kano
Jami'an tsaron Najeriya a inda aka kai harin Bon a Unguwar Sabon gari a Kano REUTERS/Stringer
Talla

Wakilin RFI Hausa a Kano Abubakar Issa Dandago yace an kai harin ne a kan titin Zungeru a unguwar Sabon gari.

Kakakin rundunar ‘Yan Sanda Frank Mba yace an jefa bom din ne a kan hanya, a harabar Mujami’ar mabiya darikar Katolika, inda Mayakan Boko Haram suka taba kai hari.

Wannan harin na zuwa ne duka sa’o’I biyu, bayan an kai wani harin bom a unguwar Nasarawa a garin Kano, amma Dandago yace harin bai shafi kowa ba.

A Jajibirin Sallah rundunar 'Yan sanda tace ta yi nasarar kwance wasu bama bamai da aka dasa a cikin wata Mota kirar Peugeot a kusa da Masallacin Isyaka Rabi'u.

Yanzu haka ‘Yan sanda sun cafke mutane uku da ake zargin sun kai hare haren a yau Lahadi da musulmi ke bikin Sallah.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.