Burkina Faso
Gwamnatin kasar Burkina Faso ta biya bukatan sojoji masu bore
Shugaban kasar Burkina Faso Blaise Compaore ya rusha gwamnatinsa, tare da nada sabon babban habsan soja, bayan bore da wasu sojoji suka yi.Manyan sakatarorin ma’aikatu zasu tafiyar aiyuka kafin nada sabbin ministoci. Yayin da Kanar Hobere Traore ya zama babban habsaon sojan kasar, inda zai maye gurbin Janar Dominique Djindjere.Ranar Alhamis sojoji kasar ta Burkina Faso suka fara bore Ouagadougou babban birnin kasar, kuma yanzu an bayyana biya musu bukatunsu. Tuni zaman lafiya ya sake komawa birnin, kamar yadda shaidun gani da ido suka tabbatar.
Wallafawa ranar: