Isa ga babban shafi

Jamus ta fitar da kanta daga jerin kasashe masu karfin nukiliya

Jamus ta kashe na’urorin inganta makamashin nukiliyarta 3  da suka saura a kokarin da take na daina amfani da makamashi mai gurbata muhalli, tare da lalubo mafita a  game da karancinsa da yakin Ukraine ya haddasa.

Shugaban gwamnatin Jamus, Olaf Scholz.
Shugaban gwamnatin Jamus, Olaf Scholz. AP - Geert Vanden Wijngaert
Talla

A yayin da akasarin kasashen yamma ke kokarin kara kudaden da suke kashewa a bangaren makamashin nukiliya, Jamus ta kawo karshen amfani  da wannan makamashi tun da wuri.

Jim kadan bayan karfe 12 na daren Asabar, kamfann RWE mai kula da makamshin a kasar ya fitar da wata sanarwar da ke cewa an kashe wadannan na’urori.

Tun a shekarar 2002 kasar da ta fi karfin arziki a nahiyar Turai ta fara tunanin yin watsi da makamashin nukiliya, amma a shekarar 2011 gwamnatin Angela Merkel ta kara azama a game da shirin, biyo bayan hatsarin tashar nukiliyar Fukushima a Japan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.