Mu Zagaya Duniya
Matakin hadin gwiwar da Nijar ,Mali da Burkina Faso suka dauka, na sanar da ficewa daga ECOWAS
Wallafawa ranar:
Kunna - 19:58
Daga cikin muhimman labarun makon jiya da shirin ya sake waiwaya domin bitarsu akwai, matakin hadin gwiwar da Nijar da Mali da kuma Burkina Faso suka dauka, na sanar da ficewa daga kungiyar ECOWAS.Sai kuma sake karya darajar Naira da gwamnatin Najeriya ta yi, karo na biyu cikin watanni 8.A Turai kuwa, za a ji yadda zanga-zangar manoma ta bazu zuwa sassan nahiyar saboda adawa da wasu sauye-sauyen mahukuntan kasashen yankin da suka ce ba za su lamunta ba.