Isa ga babban shafi
Nijar

Kamfanoni masu zaman kansu na fuskantar matsalar durkushewa a Nijar

Jamhuriyar Nijar kamar sauran kasashe maso tasowa na nahiyar Afirka na fuskantar durkushewar kamfanoni masu zaman kansu, saboda dalilai daban daban, abinda ke yi wa tattalin arzikinta illa, musamman wajen hana jama’a samun aikin yi da kuma dakile kudaden shigar da gwamnati ke samu da kuma hada hadar kasuwanci. 

Wani sashin Yamai, babban birnin Jamhuriyar Nijar.
Wani sashin Yamai, babban birnin Jamhuriyar Nijar. © Wikipedia
Talla

Yayin da masana ke zargin shugabannin kamfanonin da rashin kwarewa wajen tafiyar da su, wasu masu kamfanonin na zargin gwamnati saboda yawan harajin da ake dora musu da kuma tsadar makamashi. 

Salissou Issa ya duba mana lamarin daga Maradi, kamar yadda za a ji a rahotonsa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.