KADUNA /TAÁDDANCI
A Najeriya barazanar mayakan Ansaru na ci gaba da yin kamari a jihar Kaduna
A Najeriya, baya ga matsalar ‘yan bindiga da sace mutane domin karbar kudin fansa da ke addabar yankin Birnin gwari na jihar Kaduna, yanzu haka, wata matsala ta sake kunno kai a yankin, inda ‘yan kungiyar Ansaru ke kara karfi, lamarin da ya jefa al’ummar yankunan da abin ya shafa cikin tsoro da fargaba, har suna yin kira ga gwamnati da ta dauki mataki. Daga Kaduna, ga rahoton da Aminu Sani Sado ya aiko mana.
Wallafawa ranar:
Kunna - 01:32