Isa ga babban shafi

Najeriya: 'Yan bindiga sun sace mutane 1,789 a Kaduna cikin watanni 6

Gwamnatin jihar Kaduna dake Najeriya, ta ce adadin mutane da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a jiyar sun kai 1,789 a cikin watanni shida, yayin da jami’an tsaro suka yi nasarar kashe ‘yan bindiga 161 tare da kame da dama daga cikin su cikin watannin.

Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gidan  jihar Kaduna Samuel Aruwan yayin gabatar da rahoton tsaro karo na biyu da na uku na shekarar 2022. 04/11/222
Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gidan jihar Kaduna Samuel Aruwan yayin gabatar da rahoton tsaro karo na biyu da na uku na shekarar 2022. 04/11/222 © kaduna state
Talla

Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gidan  jihar Kaduna Samuel Aruwan ne ya bayyana hakan yayin da yake gabatar da rahoton tsaro, inda yace hare-haren ‘yan bindigar ya kashe fararen hula 285 a tsawon lokacin na watanni shidan yayin da batagarin suka kuma sace shanun da yawansu ya kai 1 da 133.

A cewarsa daga ranar 1 ga watan Yulin da ya gabata zuwa Satumba sai da ‘yan bindigar suka sace mutanen da yawansu ya kai 804 da kaso mai yawa a tsakiyar jihar inda aka saci mutane 508 a lokacin kadai.

Kwamishinan Ya ce an kama mutane 654 da ake zargi a tsawon lokacin da ake binciken.

Barazana ga zabe

A halin da ake ciki, gwamnan jihar Kaduna, Nasir el-Rufai, ya ce tashe tashen hankula a yankin Arewa maso Yamma na da hadari ga zaben 2023 da kidayar jama’a idan ba a magance matsalar ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.