Isa ga babban shafi

Yan bindiga sun sake sakin bidiyon fasinjojin jirgin kasan da suka sace

Yan bindigar da suka yi garkuwa da fasinjojin jirgin kasar da suka tare tsakanin Abuja zuwa Kaduna sun sake sakin wani faifan bidiyo mai dauke da fasinjojin suna rokon gwamnati da ta biya musu bukata domin kubutar da su.

Wasu daga cikin makaman da yan bindiga suka mika zuwa hukuma a Zamfara.
Wasu daga cikin makaman da yan bindiga suka mika zuwa hukuma a Zamfara. REUTERS/Goran Tomasevic/File Photo
Talla

Daga cikin wadanda suka yi jawabi a bidiyon mai dauke da Yan bindigar dake rataye da makamai a bayan fasinjojin, ta bayyana kan ta a matsayin dalibar Jami’ar Jihar Kaduna inda ta bukaci a taimaka wajen ceto su.

Wata kuma ta bayyana kan ta a matsayin Gladys Tony wadda take aiki a ma’aikatar tsaro, yayin da wasu kuma suke zazzaune a kasa, wasu kuma a kwance.

A cikin bidiyon farko da suka saki dai, 'yan bindigar sun yi barazanar kashe dukkanin mutanen dake tsare a hannunsu idan gwamnatin Najeriya ta kasa biya musu bukatunsu, wadanda suka ce ta san dasu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.