Isa ga babban shafi
Nigeria - Kaduna

Jami'ar Ahmadu Bello ta gudanar da zanga-zangar kwace mata filaye

Kungiyar Malaman Jami’o’in Najeriya ASUU reshen Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zaria ta gudanar da zanga zangar kin amince wa da kwace wani fili mallakin jami’ar da ya kai  kadada100 da gwamnatin jihar Kaduna ta yi domin raba wa alumma da ke bukatar yin gini.

Jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria
Jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria © Daily Trust
Talla

Shugaban kungiyar, Haruna Jibril  ya ce wannan abin damuwa ne matuka saboda haka suna kira ga gwamna Nasir E-lrufai da ya gaggauta jenye wannan mataki domin filin makarantar na al’umma ne baki daya. Sai dai a nata bangare, gwamnatin jihar ta ce rashin yin amfani da filin yadda ya kamata tare da sayar da wasu filaye da jami’ar ta yi ne, ya sa ta  kwacewa. Wakilinmu daga Kaduna, Aminu Sani Sado ya aiko mana wannan rahoto.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.