Isa ga babban shafi

Akwai yiwuwar farfado da yajejeniyar nukiliyar Iran - Grossi

Shugaban hukumar kula da makamashin nukiliya ta majalisar dinkin duniya, Rafael Grossi ya ce tattaunawa mai tasiri da ya yi da jami’an Iran na iya share fagen farfado da yarjejeniyar nukiliyar 2015.

Shugaban hukumar  nukiliyar MDD, Rafael Grossi da  na Iran Mohammad Eslami, a birnin Téhéran, la rana 3 ga watan Maris, 2023.
Shugaban hukumar nukiliyar MDD, Rafael Grossi da na Iran Mohammad Eslami, a birnin Téhéran, la rana 3 ga watan Maris, 2023. via REUTERS - WANA NEWS AGENCY
Talla

Grossi ya bayyana haka ne a wani taron manema labarai da ya  yi tare da shugaban hukumar kula da makamashin nukiliyar Iran Mohammad Eslami a birnin Tehran.

Ziyarar yini 2 da Grossi ya  kai Iran na zuwa ne a daidai lokacin da tattaunawar farfado da yarjejejniyar nukiliyar 2015 tsakanin Iran da manyan kasashen duniya  ta ruguje, duk da cewa akwai alwashin sauke takunkuman karayar tattalin arziki da aka kakaba  wa Iran idan aka samu nasara.

A shekarar 2018 Amurka ta janye daga wannan yarjejeniyar nukiliya, kana ta sake kakaba wa Iran takunkumai,  lamarin da ya sa Iran ta mayar da martini ta wajen  dakatar da aiwatar da alkawuran da ta dauka a karkashin yarjejeniyar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.