Isa ga babban shafi
Japan

Japan ta yi nadama ga kasashen da ta ba wahala a yakin duniya na biyu

Firaministan Japan Shinzo Abe ya ce kasarsa ta yi nadama ga ta’asar da ta aikatawa kasashen Asiya, shugaban ya fadi haka ne a jawabinsa na cika shekaru 70 da kawo karshen yakin duniya na biyu da aka samu galaba akan kasar.

Firaministan Japan Shinzo Abe
Firaministan Japan Shinzo Abe REUTERS/Toru Hanai
Talla

Jawabin Shugaban dai dama ce ga Japan na farfado da dangantakarta da China da kuma Korea ta Kudu, kasashen da suka sha wahala a hannunta a lokacin yakin duniya na biyu.

Firaministan ya fadi kalamai, na neman gafara da ta’asar da Japan ta aikata a cikin jawabinsa.

Dakarun Japan dai sun mika wuya a lokacin da aka samu galaba akan su a 1945.

China tace sama da mutanen kasarta Miliyan 20 Japan ta kashe.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.