Isa ga babban shafi

Japan tace har yanzu ba a kulla yarjejeniya ba don sako mutanen da ISIS ta kama

Hukumonin kasar Japan sun ce har yanzu ba a kai ga kulla yarjejeniya da ‘yan kungiyar ISIS ba, da suka yi barazanar hallaka wani matukin jirgin sama da kasar Jordan Maaz al-Kassasbeh, da kuma dan Jaridar kasar ta Japan Kenji Goto. Ministan harkokin wajen kasar Yasuhide Nakayama, dake jagorantar tawaggar agajin gaggawan kasar, ya shida wa ‘yan jarida a birnin Amman na kasar Jordan cewa har yanzu ba a sako mutanen 2 ba.Can a birnin Tokyo kuwa, yau Asabar wani babban jami’in gwamnatin Japan Hiroshige Seko, dake a matsayin na hannun dama Fraiminista Shinzo Abe, yace suna dakon bayanai kan halin da mutanen ke ciki.Jiya wa’adin da mayakan na ISIS suka bayar ya cika, inda suka nemi a sako wata mace ‘yar kunar bakin wake dake tsare a gidan yarin kasar Jordan ko su kashe mutanen 2.A makon da ya gabata mayakan na ISIS suka fille kan wani dan kasar Japan mai suna Haruna Yukawa. 

Gidajen talibijin din kasar Japan na nuna hotunan Kenji Goto
Gidajen talibijin din kasar Japan na nuna hotunan Kenji Goto REUTERS/Yuya Shino
Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.