Isa ga babban shafi
OPEC

Saudiya ba za ta rage yawan Man da ta ke fitarwa ba

Kasashen Larabawa masu arzikin mai sun ce ba zasu rage adadin man da suke fitarwa ba a kasuwa saboda faduwar farashin man a kasuwannin duniya, duk da wasu kasashen da ba su cikin kungiyar OPEC sun nemi rage yawan danyen man da ake fitarwa.

Sarki Abdallah na Saudiya da Ministan harkokin wajen kasar Saud al-Faisal da Attajiri dan gidan Yarima Alwaleed bin Talal
Sarki Abdallah na Saudiya da Ministan harkokin wajen kasar Saud al-Faisal da Attajiri dan gidan Yarima Alwaleed bin Talal Forbes
Talla

Saudiya da Kuwait masu arzikin mai sun ce ba za su rage yawan adadin man da suke fitarwa ba, yayin da kuma Daular Larabawa da Iraqi suka yi watsi da kiran da ake yi wa OPEC akan ta kira taron gaggawa game da faduwar farashin mai.

Amma a wani taron makamashi da aka gudanar a birnin Abu Dhabi na Daular Larabawa, Ministan mai na Saudiya Ali al Naimi ya jaddada cewa Saudiya ba zata rage yawan adadin man da ta ke fitarwa ba, kuma Ministan Kuwait ya amince da hakan.

An dai samu faduwar farashin danyen mai ne a kasuwannin duniya da kusan kashi 50 tun a watan Yuni, saboda wadatuwar man a kasuwa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.