Cuba ta aika da tallafi ga mutanen Gaza
Hukumomin kasar Cuba sun aike da kayan agajin da suka hada da magunguna da kayan aikin asibiti, don tallafawa mutanen da yaki ya daidaita a yankin Gaza. Wani shafin Internet mallakin kasar ta Cuba ya bayyana cewa, jami’an gwamnatin kasar ne suka mika kayan agajin ga wakilan Falasdinawa a birnin Alkahira na kasar Masar.
Wallafawa ranar:
A ranar 26 ga watan Agusta kasar Isra’ila da kungiyar Falasdinawa ta Hamas, suka amince da kawo karshen yakin da aka shafe makwanni bakwai ana gwabazawa, inda aka samu hasarar rayukan Falasdinawa fiye da mutane 2,100 a zirin Gaza, akasarinsu fareren hula.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu