Iraq
Dubban Jama'a Na Cikin Wani Hali A Yazidi Na Kasar Iraki
Masu ayyukan sa idanu na Majalisar Dinkin Duniya gameda rikicin kasar Iraki sun bayyana bukatar kai dauki cikin gaggawa ga alummar Yazidi gudun kada lamarin ya kai ga an yi masu kisan kiyashi.Dubban mabiya wasu addinai na chan sun makale a tsaunukan yankin dake Arewa maso Yammacin Iraki babu ruwa da abinci, bayan fatattakansu da masu tsananin kishin Islama suka yi.Masu sa idanun na cewa mata da kananan yara na cikin mummunar hali a inda suke fakewa.
Wallafawa ranar: