Isa ga babban shafi
Syria

‘Yan adawa a Syria sun tube kwamandansu

Gwamnatin ‘Yan adawa a Syria ta tube kwamandan mayakan da ke yaki da dakarun Bashar al Assad akan zargin yin rub da ciki da kudadensu. Wannan na zuwa ne a yayin da Amurka ke shirin ware kudi dala Miliyan 500 domin bayar da horo ga ‘Yan tawayen.

Wasu Mayakan Kungiyar al Nusra suna rike da makamai a wani gida da suke buya a yankin Aleppo a Syria
Wasu Mayakan Kungiyar al Nusra suna rike da makamai a wani gida da suke buya a yankin Aleppo a Syria REUTERS/Ammar Abdullah
Talla

Sanarwar da ‘Yan tawayen suka fitar a Facebook, Shugabansu Ahmad Tohme yace sun kaddamar da bincike akan Kwamandan dakarun ‘Yan tawayen Janar Abdelilah al Bashir.

Sanarwar kuma na zuwa a dai dai lokacin da Shugaban Amurka Barack Obama ya nemi Majalisa ta amince da kudi dala Miliyan 500 domin bayar da horo tare dab a ‘Yan tawayen na Syria makamai.

Akwai tattaunawa da Sakateren Harakokin Wajen Amurka John Kerry zai gudanar tare da ‘Yan tawayen Syria da mahukuntan Saudi Arebiya a birnin Jeddah.

An shafe tsawon shekaru uku ‘Yan tawaye suna yakin kawo karshen mulkin Bashar Al Assad a Syria.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.