Isa ga babban shafi
Afghanistan

Ban Ki-moon ya yaba da zaben Afghanistan

Sakataren Majalisar Dinkin Duniya Ban Ki-moon ya yaba da yadda aka gudanar da zaben shugaban kasa a kasar Afghanistan tare da mika sakon taya murna ga mutanen kasar akan samun nasarar gudanar da zaben da kungiyar Taliban ta yi barazanar haramtawa.

Mata suna layin kada kuri'arsu a zaben kasar Afghanistan
Mata suna layin kada kuri'arsu a zaben kasar Afghanistan REUTERS/Zohra Bensemra
Talla

Mr. Ban ya jinjinawa shugabannin hukumar da suka gudanar da zaben tare da fatar zasu kamanta gaskiya wajen fadin sakamakon da al’umma suka zaba.

Sai dai akwai ‘Yan takara a zaben shugaban kasar da suka yi korafin an yi magudi a zaben.

Hukumar zaben Afghanistan tace ta samu korafe-korafe a game da zaben 1,200.

Barazanar kungiyar Taliban na kai hare haren bama bamai a runfunan zabe bai hanawa Miliyoyan mutanen kasar fitowa kada kuri’arsu ba domin zaben wanda zai gaji Hamid Karzai.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.