Netanyahu ya soki kasashen duniya kan kasar Iran
Fira Ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya soki kasashen duniya kan abinda ya kira munafincin su kan kasar Iran, yayin da yake bayyana makaman da kasar ta aike da su zuwa Yankin Gaza.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Netanyahu wanda yake jawabi a gaban makaman, ya ce abin bakin ciki ne yadda duniya ta ki amincewa da barazanar Iran, ganin yadda take ci gaba da taimakawa ayyukan ta’addanci a duniya.
Israila na zargin Iran da aikewa da makamai wa kungiyar Hamas a Yankin Gaza yayin da take ci gaba da nuna adawa da zaman sasantawar da ake da Iran da manyan kasashen duniya game da makamashin nukiliyanta.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu