‘Yan gudun Hijira 18 suka mutu a hatsarin Kwale-kwalen kasar Turkiyya
Akalla mutane 18 da ake zaton cewar ‘yan gudun Hijira ne, suka mutu, bayan da Jirgin Kwale-kwalen da suke ciki ya kife a cikin Ruwa.
Wallafawa ranar:
Wannan hatsarin dai ya auku ne a yankin Ruwan Tsibirin Caicos na yankin Karebiyan.
Hatsarin kuma ya auku ne da sanyin Safiyar Ranar kirsimeti, bayan da ‘yan sanda suka keace Jirgin da ke makare da mutane, koda yake an bayyana ceto akalla mutane 32 daga cikin Fasinjojin Jirgin.
Yanzu haka dai ana can ana lalaben sauran Gawawwakin wadanda suka mutu, a yayin da wani Jirgin saman kasar Amurka ke ta sintiri domin taimakawa masu aikin ceton gano inda sauran mutanen suke.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu