Isa ga babban shafi
RIKICIN ECOWAS

Ficewar Nijar da Mali da Burkina Faso na iya rura wutar matsalolin yankin - Masana

Kwararru sun yi gargadin cewa barazanar da ake fuskanta saboda matakin Nijar, Mali da Burkina Faso na daura aniyar ficewa daga cikin kungiyar ECOWAS ka iya zarta yadda ake tunani.

Wani bangare mai fadin gaske a yankin Sahel
Wani bangare mai fadin gaske a yankin Sahel AP - Ben Curtis
Talla

Masanan sun ce muddin aka gaza warware matsalar ta fuskar tattaunawa, to fa baya ga matsalar tsaro, ficewar kasashen uku daga ECOWAS, ka iya rusa hada-hadar kasuwancin kusan dala miliyan 150 da ke gudana duk shekara a tsakanin kasashen yammmacin Afirka.

Farfesa Kamilu Sani Fagge masanin siyasar kasa da kasa a Najeriya da ke Jami’ar Bayero a Kano, ya tabbatar wa sashin Hausa na RFI cewar, babu kuskure a gargadin kwararrun, la’akari da yanayin da yankin yammacin Afirka ke ciki.

02:02

Farfesa Kamilu Sani Fagge kan aniyar Mali da Burkina Faso da Nijar ta neman ficewa daga cikin kungiyar ECOWAS

Yanzu haka dai akwai batutuwa da dama da suka jefa miliyoyin mutane ‘yan kasashen kungiyar ta ECOWAS mai manbobi 15 cikin zurfin tunani, musamman kan yadda makomarsu za ta kaya idan har lamurra suka rincabe kamar yadda ake fargaba.

Wani taron kasashen kungiyar ECOWAS a Abuja babban birnin Najeriya a ranar 10 ga Disamban shekarar 2023.
Wani taron kasashen kungiyar ECOWAS a Abuja babban birnin Najeriya a ranar 10 ga Disamban shekarar 2023. AFP - KOLA SULAIMON

Daga cikin muhimman batutuwan da makomarsu ke daukar hankali dai akwai matsayin miliyoyin mutanen da ke zaune a kasashe makwaftansu da ke yammacin nahiyar ta Afirka, albarkacin cewa babu bukatar takardun biza da kuma bai wa mutane damar samun guraben aiki a kasashen da ba nasu ba, a tsakanin manbobin kungiyar ECOWAS.

Ga misali, wata kididdiga ta nuna cewar a Ivory Coast kadai, akwai ‘yan kasashen Burkina Faso da Mali da kuma Jamhuriyar Nijar sama da miliyan 5 wadanda ke aiki.

A bangaren makwaftaka kuwa, Nijar na da iyakar da tsawonta ya kai akalla kilomita dubu 1,500 tsakaninta da Najeriya.

Sai kuma bangaren kasuwanci inda kashi 80 cikin 100 na hada-hadar kasuwancin da al’ummar Nijar ke yi na gudana ne tsakaninsu da Najeriya, alkaluman da Abba Sadik shugaban wata  cibiyar bincike mai suna CIRES da ke birnin Paris ya  tabbatar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.