Isa ga babban shafi

Sama da mutum miliyan biyu ne ke fama da lalurar kwakwalwa a Ghana - WHO

Wani rahoto da Hukumar Lafiya ta Duniya ta fitar, ya ce akwai mutane fiye da milyan 2 da dubu 400 da ke fama da lalurar tabin hankali a kasar Ghana kawai. 

Wasu alkalumma sun nuna cewa kashi 25 zuwa 30 na al'ummar kasar na fama da matsalolin da ke da nasaba da kwakwalwa.
Wasu alkalumma sun nuna cewa kashi 25 zuwa 30 na al'ummar kasar na fama da matsalolin da ke da nasaba da kwakwalwa. © punch.com
Talla

Rahoton ya ce wannan matsala na kara ta’azzara saboda karancin jami’n kiwon lafiyar da ke da kwarewa a wannan kula da masu tabin hankali a kasar. 

A watan Fabrairu ne, kungiyar kare hakkin bil'adama ta Human Rights Watch ta shawarci gwamnatin Ghana da ta kawo karshen irin yadda ake tsare da mutane masu tabin hankali a kasar. 

Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken rahoton Abdallah Sham’un Bako.

A yayin taron kungiyar da aka yi a shekarar 2017, gwamnatin Ghana ta goyi bayan shawarwari 10 cikin 11 da suka shafi 'yancin masu bukata ta musamman, ciki har da hana, cin zarafin bil'adama asibitocin kula da masu lalurar kwakwalwa.

A cikin Nuwamban 2022, Human Rights Watch ta gano fiye da mutane 60, ciki har da wasu yara, daure cikin sarka, da kuma wadanda aka killace a cikin keji yayin da ake azabtar da su da yunwa da kuma rashin tsaftar muhallin da aka ajiye su.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.