Isa ga babban shafi
Champions League

Chelsea ta nemi a kare rayukan magoya bayanta a Turkiya

Kungiyar Galatasaray zata karbi bakuncin Chelsea a birnin Istanbul inda Dideiar Drgba na Cote d’Ivoire zai hadu da tsoffin abokan wasan shi. Sai dai kuma kungiyar Chelsea ta tabbatar da labarin wani hari da aka kai wa magoya bayanta guda biyu a birnin Istanbul kafin fafatawarta da Galatasaray.

Kocin Chelsea Jose Mourinho
Kocin Chelsea Jose Mourinho REUTERS/Eddie Keogh
Talla

Yanzu haka zanga-zanga ce ake ci gaba da gudanarwa a kasar Turkiya, kuma akwai bukatar da kungiyar Chelsea ta gabatar ga Jami’an tsaron kasar domin kare rayukan magoya bayanta a filin wasa.

An dai taba kashe wasu magoya bayan kungiyar Leeds United guda biyu a birnin Istanbul a lokacin da zata kara da Galatasaray a 2000.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.