Tawagar kungiyar ECOWAS ta gana da shugabannin gwamnatin sojin Nijar da zummar tattauna yadda za'a mayar da mulki ga fararen hula kamar yadda kungiyar ta bukata da niyar cirewa kasar takunkumin karya tattalin arzikin da aka kakaba mata. Bayan ganawar da aka yi tsakanin tawagar dake karkashin jagorancin ministan harkokin wajen Togo Robert Doussey da Firaministan Nijar Ali Lamine Zein, ministan yace bangarorin biyu sun cimma matsayar da zasu gabatarwa shugabannin ECOWAS.
AbdoulkarimIbrahim Shikal ya tattauna da Ambasada Abubakar Chika, tsohon jakadan Najeriya a Iran. Ga yadda zantawarsu ta gudana.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu