Juyin mulki na gurgunta shirin kungiyar Tarayyar turai na tabbatar da tsaro a Sahel
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:28
Kungiyar kasashen Turai ta EU tace ta kashe yuro miliyan 600 wajen horar da sojojin dake yankin Sahel domin kare dimokiradiyya, amma kuma abin takaici shirin bai yi nasara ba, sakamakon yadda sojoji suka dinga gudanar da juyin mulki.
Shugaban kula da harkokin diflomasiyyar kungiyar, Joseph Borrell yace a cikin shekaru 10 sun horar da jami’an tsaro da na sojin da suka kai dubu 50, cikin su harda na Nijar da Mali.
Dangane da wannan matsayi Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Bashir Nuhu Mabai na Jami’ar Gwamnatin Tarayya dake Katsina, kuma ga yadda zantawar su ta gudana.
Danna alamar saurare don jin cikakken shirin
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu