Rahotanni daga Kaduna a arewa maso yammacin Najeriya sun ce ‘Yan ta’adda da sauran masu aikata miyagun laifuka na kusantar birnin Kaduna, inda a dalilin hakan ake samun karuwar hare-hare da sace-sacen mutane a garuruwa da kauyukan da ke kusa da babban birnin jihar.
Majiyoyin tsaro sun ce ‘yan ta’addan da ke addabar sassan da ke kusa da manyan yankunan birnin Kaduna sun shiga rudani ne saboda hare-hare da sojoji ke kaiwa maboyarsu a cikin dazuzzuka, abinda ya sanya su matsawa kusa da garuruwa don gujewa kama su, a lokaci guda kuma suke ci gaba da tafka ta’asa.
Kan wannan matsala muka tattauna da wani mazauni a daya daga cikin yankunan da ke fuskantar barzanar tsaron.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu