Isa ga babban shafi

Najeriya: An kashe mutane 645 cikin watanni shida a Kaduna

Gwamnatin jihar Kaduna dake Najeriya tace, hare-haren kungiyoyi masu dauke da makamai sun kashe mutane 645 a jihar cikin watanni shida, wato daga  watan Janairu zuwa Yuni wannan shekara ta 2022.

Jami'an tsaro a jihar Kaduna
Jami'an tsaro a jihar Kaduna REUTERS/Stringer
Talla

Gwamnatin jihar ta bayyana hakan ne cikin wani rahoton tsaro kan tashe tashen hankula a jihar da ta fitar  ranar Juma’a.

Rahoton ya bayyana cewa an kashe adadin wadan nan mutane ne a hare-haren ta'addanci da fadan kabilanci da kuma na ‘yan fashin daji.

Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na jihar, Samuel Aruwan, a wata sanarwa da ya fitar ya ce kusan kashi daya bisa uku na wadanda aka kashe (234) an kashe su ne a Kudancin Kaduna.

“A cikin watanni shida na farkon shekarar 2022, mutane 645 ne suka rasa rayukansu a irin wannan yanayi a fadin jihar; 234 daga cikin wadannan sun faru ne a yankin Kudancin Kaduna,” in ji Mista Aruwan a wani taron gabatar da rahotannin zaman lafiya a tsakanin addinai.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.