Gwamnatin Kaduna ta tsawaita dokar hana hawa babura
Bayan kwashe watanni uku da haramta hawa babur a fadin jihar Kaduna a tarayyar Najeriya, yanzu haka gwamnatin jihar bayan nazarin da tayi dangane da bukatar jamian tsaro, ta sake tsawaita dokar har sai Baba ta gani.
Wallafawa ranar:
Kunna - 01:26
A cikin watan Oktoban shekarar 2021 ne Al'umma da dama a jihar Kaduna da ke Najeriya suka koka dangane da matakan da gwamnatin jihar ta dauka na dakile aikin 'Yan ta'adda a jihar inda su ke ganin cewa matakan sunyi tsauri da yawa, kuma suke bukatar a sassauta. A lokacin ne gwamnatin jihar ta hana hawa babura a fadin jihar har na tsawon watanni uku tare kuma katse layukan sadarwa a wasu sassan jihar
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu