Kaduna na shirin sallamar daruruwan malaman makaranta
Gwamnatin jihar Kaduna ta Najeriya ta sanar da shirinta na sallamar malaman makaranta har su 233 saboda amfani da kwalin shedar kammala karatu na bogi.
Wallafawa ranar:
Shugaban Kwamitin Zartaswa na Hukumar Bunkasa Ilimin Bai-Daya a jihar, Alhaji Tijjani Abullahi ya bayyana haka a ranar Alhamis a yayin wani taron manema labarai.
Abdullahi y ace, sun gano wannan adadin ne bayan kaddamar da wani aikin tantance sahihancin kwalayen malamai a cikin watan Afrilun bara.
Jami’in ya ce, sun yi haka ne da zummar tabbatar da cewa, malaman na da kwarewar da ake bukata ta karantawa.
Gwamnatin jihar za kuma ta gabatar da wadannan masu kwalayen bogin a gaban shari’a domin fuskantar hukunci kamar yadda Abdullahi ya bayyana.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu