Bakonmu a Yau
Za mu zartas da hukunci mai tsauri kan masu tada zaune tsaye a Kaduna - El Rufa'i
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:27
Gwamnan Kaduna Malam Nasiru El-Rufai ya gana shugabannin rundunonin tsaro a jihar kan matsalar hare-haren ‘yan bindiga a wasu yankunan kudancin jihar, abinda ya kai ga kafa dokar hana fita a wasu kananan hukumomi.Gwamnan sha alwashin hukunta duk wanda aka samu da hannu wajen tunzura rikicin kabilanci, abinda yace na daya daga cikin batutuwan dake rura wutar matsalar tsaro a Kudancin Kaduna.Wakilinmu Aminu Sani Sado na daga cikin ‘yan Jaridun da gwamnan ya gana da su bayan jagorantar taron gaggawar.