FIFA
FIFA ta dakatar da Najeriya
Hukumar FIFA ta dakatar da hukumar kwallon Najeriya saboda katsalandan da gwamnatin kasar ke yi wa sha’anin kwallon kafa. Wannan kuma na zuwa ne bayan wata kotu a Najeriya ta dakatar shugabannin hukumar NFF, inda nan take kuma gwamnati ta nada shugabannin rikon kwarya.
Wallafawa ranar:
Talla
Wannan al’amari duka duka na zuwa ne bayan Faransa ta kori Najeriya a gasar cin kofin duniya a Brazil.
Idan dai har FIFA ba ta dage haramcin ba, matakin zai haramta wa Najeriya buga gasar cin kofin duniya ta mata ‘Yan kasa da shekaru 20 da za’a gudanar a kasar Canada a watan gobe.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu